Select surah Select surah 1 Al-Fatihah ( The Opening ) [7] 2 Al-Baqarah ( The Cow ) [286] 3 Al-Imran ( The Famiy of Imran ) [200] 4 An-Nisa ( The Women ) [176] 5 Al-Maidah ( The Table spread with Food ) [120] 6 Al-An'am ( The Cattle ) [165] 7 Al-A'raf (The Heights ) [206] 8 Al-Anfal ( The Spoils of War ) [75] 9 At-Taubah ( The Repentance ) [129] 10 Yunus ( Jonah ) [109] 11 Hud [123] 12 Yusuf (Joseph ) [111] 13 Ar-Ra'd ( The Thunder ) [43] 14 Ibrahim ( Abraham ) [52] 15 Al-Hijr ( The Rocky Tract ) [99] 16 An-Nahl ( The Bees ) [128] 17 Al-Isra ( The Night Journey ) [111] 18 Al-Kahf ( The Cave ) [110] 19 Maryam ( Mary ) [98] 20 Taha [135] 21 Al-Anbiya ( The Prophets ) [112] 22 Al-Hajj ( The Pilgrimage ) [78] 23 Al-Mu'minoon ( The Believers ) [118] 24 An-Noor ( The Light ) [64] 25 Al-Furqan (The Criterion ) [77] 26 Ash-Shuara ( The Poets ) [227] 27 An-Naml (The Ants ) [93] 28 Al-Qasas ( The Stories ) [88] 29 Al-Ankaboot ( The Spider ) [69] 30 Ar-Room ( The Romans ) [60] 31 Luqman [34] 32 As-Sajdah ( The Prostration ) [30] 33 Al-Ahzab ( The Combined Forces ) [73] 34 Saba ( Sheba ) [54] 35 Fatir ( The Orignator ) [45] 36 Ya-seen [83] 37 As-Saaffat ( Those Ranges in Ranks ) [182] 38 Sad ( The Letter Sad ) [88] 39 Az-Zumar ( The Groups ) [75] 40 Ghafir ( The Forgiver God ) [85] 41 Fussilat ( Explained in Detail ) [54] 42 Ash-Shura (Consultation ) [53] 43 Az-Zukhruf ( The Gold Adornment ) [89] 44 Ad-Dukhan ( The Smoke ) [59] 45 Al-Jathiya ( Crouching ) [37] 46 Al-Ahqaf ( The Curved Sand-hills ) [35] 47 Muhammad [38] 48 Al-Fath ( The Victory ) [29] 49 Al-Hujurat ( The Dwellings ) [18] 50 Qaf ( The Letter Qaf ) [45] 51 Adh-Dhariyat ( The Wind that Scatter ) [60] 52 At-Tur ( The Mount ) [49] 53 An-Najm ( The Star ) [62] 54 Al-Qamar ( The Moon ) [55] 55 Ar-Rahman ( The Most Graciouse ) [78] 56 Al-Waqi'ah ( The Event ) [96] 57 Al-Hadid ( The Iron ) [29] 58 Al-Mujadilah ( She That Disputeth ) [22] 59 Al-Hashr ( The Gathering ) [24] 60 Al-Mumtahanah ( The Woman to be examined ) [13] 61 As-Saff ( The Row ) [14] 62 Al-Jumu'ah ( Friday ) [11] 63 Al-Munafiqoon ( The Hypocrites ) [11] 64 At-Taghabun ( Mutual Loss & Gain ) [18] 65 At-Talaq ( The Divorce ) [12] 66 At-Tahrim ( The Prohibition ) [12] 67 Al-Mulk ( Dominion ) [30] 68 Al-Qalam ( The Pen ) [52] 69 Al-Haaqqah ( The Inevitable ) [52] 70 Al-Ma'arij (The Ways of Ascent ) [44] 71 Nooh [28] 72 Al-Jinn ( The Jinn ) [28] 73 Al-Muzzammil (The One wrapped in Garments) [20] 74 Al-Muddaththir ( The One Enveloped ) [56] 75 Al-Qiyamah ( The Resurrection ) [40] 76 Al-Insan ( Man ) [31] 77 Al-Mursalat ( Those sent forth ) [50] 78 An-Naba' ( The Great News ) [40] 79 An-Nazi'at ( Those who Pull Out ) [46] 80 Abasa ( He frowned ) [42] 81 At-Takwir ( The Overthrowing ) [29] 82 Al-Infitar ( The Cleaving ) [19] 83 Al-Mutaffifin (Those Who Deal in Fraud) [36] 84 Al-Inshiqaq (The Splitting Asunder) [25] 85 Al-Burooj ( The Big Stars ) [22] 86 At-Tariq ( The Night-Comer ) [17] 87 Al-A'la ( The Most High ) [19] 88 Al-Ghashiya ( The Overwhelming ) [26] 89 Al-Fajr ( The Dawn ) [30] 90 Al-Balad ( The City ) [20] 91 Ash-Shams ( The Sun ) [15] 92 Al-Layl ( The Night ) [21] 93 Ad-Dhuha ( The Forenoon ) [11] 94 As-Sharh ( The Opening Forth) [8] 95 At-Tin ( The Fig ) [8] 96 Al-'alaq ( The Clot ) [19] 97 Al-Qadr ( The Night of Decree ) [5] 98 Al-Bayyinah ( The Clear Evidence ) [8] 99 Az-Zalzalah ( The Earthquake ) [8] 100 Al-'adiyat ( Those That Run ) [11] 101 Al-Qari'ah ( The Striking Hour ) [11] 102 At-Takathur ( The piling Up ) [8] 103 Al-Asr ( The Time ) [3] 104 Al-Humazah ( The Slanderer ) [9] 105 Al-Fil ( The Elephant ) [5] 106 Quraish [4] 107 Al-Ma'un ( Small Kindnesses ) [7] 108 Al-Kauther ( A River in Paradise) [3] 109 Al-Kafiroon ( The Disbelievers ) [6] 110 An-Nasr ( The Help ) [3] 111 Al-Masad ( The Palm Fibre ) [5] 112 Al-Ikhlas ( Sincerity ) [4] 113 Al-Falaq ( The Daybreak ) [5] 114 An-Nas ( Mankind ) [6]
Select language Select language العربية English English - Yusuf Ali English - Transliteration Français Nederlands Türkçe Melayu Indonesia 中文 日本語 Italiano 한국어 മലയാളം Português Español اردو বাংলা தமிழ் České Deutsch فارسى Română Русский Svenska Shqip Azəri Bosanski Български Hausa كوردی Norwegian Polski soomaali Swahili Тоҷикӣ Татарча ไทย ئۇيغۇرچە Ўзбек ދިވެހި Sindhi
Select reciter Select reciter Abdullah Basfar Shaikh Mohammed Abdul Kareem Abdul Rasheed Sufi Ahmad Ahmad Nuaina Shaikh Mahmoud Ali al-Banna Shaikh Yaser Al-Dawsari Shaikh Saud Al-Shuraim Maher Bin Hamd Al-Muayqili Khalid Al-Qahtani Abdullah Khayyat Shaikh Salah Alhashim Abdul Wadood Maqbool Haneef Ahmad Bin Ali Al-Ajmi Fares Abbad Hani Al-Rifai Sahl Bin Zain Yaseen Ali Abdullah Jaber Muhammad Ayyob Saad Al-Gamdi Salah Bu Khater Abdullah bin Awwad Al-Juhany Shaikh AbuBakr As-Shatery Muhammad Siddiq Al-Manshawi Mahmood Khaleel Al-Husari Abdul Basit Abdus Samad AbdulAzeez al-Ahmad Abdur-Rahman as-Sudais Ali Abdur-Rahman al-Huthaify Hamad Sinan Ibrahim Al-Jibrin Muhammad al-Mehysni Saleh al Taleb AbdulBari ath-Thubaity Adel Kalbani Muhammad al-Luhaidan Salah al-Budair Mshari Alefasi
Hausa Surah As-Sajdah ( The Prostration ) - Aya count 30
تَنزِيلُ ٱلْكِتَٰبِ لَا رَيْبَ فِيهِ مِن رَّبِّ ٱلْعَٰلَمِينَ ﴿٢﴾
Saukar da Littafin bãbu shakka a gare shi, daga Ubangijin tãlikai yake.
أَمْ يَقُولُونَ ٱفْتَرَىٰهُ ۚ بَلْ هُوَ ٱلْحَقُّ مِن رَّبِّكَ لِتُنذِرَ قَوْمًۭا مَّآ أَتَىٰهُم مِّن نَّذِيرٍۢ مِّن قَبْلِكَ لَعَلَّهُمْ يَهْتَدُونَ ﴿٣﴾
Kõ sunã cẽwa (Muhammadu ne) ya ƙirƙira shi? Ã'a, shĩ ne gaskiya daga Ubangijinka, dõmin ka yi gargaɗi ga mutãne waɗanda wani mai gargaɗi bai je musu ba a gabãninka, fãtan zã su shiryu.
ٱللَّهُ ٱلَّذِى خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا فِى سِتَّةِ أَيَّامٍۢ ثُمَّ ٱسْتَوَىٰ عَلَى ٱلْعَرْشِ ۖ مَا لَكُم مِّن دُونِهِۦ مِن وَلِىٍّۢ وَلَا شَفِيعٍ ۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ ﴿٤﴾
Allah ne wanda Ya halitta sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu a cikin kwãnuka shida, sa'an nan Ya daidaita a kan Al'arshi. Bã ku da, baicin Shi, wani majiɓinci kuma babu wani maceci. Shin, bã zã ku yi tunãni ba?
يُدَبِّرُ ٱلْأَمْرَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ إِلَى ٱلْأَرْضِ ثُمَّ يَعْرُجُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍۢ كَانَ مِقْدَارُهُۥٓ أَلْفَ سَنَةٍۢ مِّمَّا تَعُدُّونَ ﴿٥﴾
Yanã shirya al'amari daga sama zuwa ga ƙasã, sa'an nan ya tãka zuwa gare Shi a cikin yini, wanda gwargwadonsa shẽkaru dubu ne ga abin da kuke lissafãwa.
ذَٰلِكَ عَٰلِمُ ٱلْغَيْبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ ٱلْعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ ﴿٦﴾
Wannan shĩ ne Masanin fake da bayyane, Mabuwãyi, Mai jinƙai.
ٱلَّذِىٓ أَحْسَنَ كُلَّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ ۖ وَبَدَأَ خَلْقَ ٱلْإِنسَٰنِ مِن طِينٍۢ ﴿٧﴾
Wanda Ya kyautata kõme, Wanda Ya halitta shi. Shi ne kuma Ya fãra halittar mutum daga lãka.
ثُمَّ جَعَلَ نَسْلَهُۥ مِن سُلَٰلَةٍۢ مِّن مَّآءٍۢ مَّهِينٍۢ ﴿٨﴾
Sa'an nan Ya sanya ɗiyansa daga wani asali na wani ruwa wulãkantacce.
ثُمَّ سَوَّىٰهُ وَنَفَخَ فِيهِ مِن رُّوحِهِۦ ۖ وَجَعَلَ لَكُمُ ٱلسَّمْعَ وَٱلْأَبْصَٰرَ وَٱلْأَفْـِٔدَةَ ۚ قَلِيلًۭا مَّا تَشْكُرُونَ ﴿٩﴾
Sa'an nan Ya daidaita shi, kuma Ya hũra a cikinsa, daga ruhinSa kuma Ya sanya muku ji, da ganunuwa da zukãta. Gõdiyarku kaɗan ce ƙwarai.
وَقَالُوٓاْ أَءِذَا ضَلَلْنَا فِى ٱلْأَرْضِ أَءِنَّا لَفِى خَلْقٍۢ جَدِيدٍۭ ۚ بَلْ هُم بِلِقَآءِ رَبِّهِمْ كَٰفِرُونَ ﴿١٠﴾
Kuma suka ce: "Shin, idan mun ɓace a cikin ƙasã, shin, lalle mu, tabbas ne munã zama a cikin wata halitta sãbuwa?" Ã'a, su game da gamuwa da Ubangijinsu kãfirai
۞ قُلْ يَتَوَفَّىٰكُم مَّلَكُ ٱلْمَوْتِ ٱلَّذِى وُكِّلَ بِكُمْ ثُمَّ إِلَىٰ رَبِّكُمْ تُرْجَعُونَ ﴿١١﴾
Ka ce: "Mala, ikin mutuwa ne. wanda aka wakkala a gare ku, shĩ ne ke karɓar rãyukanku. Sa'an nan zuwa ga Ubangijinku ake mayar da ku."
وَلَوْ تَرَىٰٓ إِذِ ٱلْمُجْرِمُونَ نَاكِسُواْ رُءُوسِهِمْ عِندَ رَبِّهِمْ رَبَّنَآ أَبْصَرْنَا وَسَمِعْنَا فَٱرْجِعْنَا نَعْمَلْ صَٰلِحًا إِنَّا مُوقِنُونَ ﴿١٢﴾
Kuma da kã gani a lõkacin da mãsu laifi suke mãsu sunkuyar da kawunansu a wurin Ubangijinsu, "Ya Ubangijinmu! Mun gani, kuma mun ji, to, Ka mayar da mu mu aikata aiki na ƙwarai. Lalle mũ mãsu yaƙĩni ne."
وَلَوْ شِئْنَا لَءَاتَيْنَا كُلَّ نَفْسٍ هُدَىٰهَا وَلَٰكِنْ حَقَّ ٱلْقَوْلُ مِنِّى لَأَمْلَأَنَّ جَهَنَّمَ مِنَ ٱلْجِنَّةِ وَٱلنَّاسِ أَجْمَعِينَ ﴿١٣﴾
Kuma dã Mun so dã Mun bai wa kõwane rai shiriyarsa to, amma magana ta tabbata daga gare Ni! Lalle ne Inã cika Jahannama daga aljannu da mutãne gabã ɗaya.
فَذُوقُواْ بِمَا نَسِيتُمْ لِقَآءَ يَوْمِكُمْ هَٰذَآ إِنَّا نَسِينَٰكُمْ ۖ وَذُوقُواْ عَذَابَ ٱلْخُلْدِ بِمَا كُنتُمْ تَعْمَلُونَ ﴿١٤﴾
To, ku ɗanɗana sabõda abin da kuka manta na haɗuwa da ranarku wannan. Lalle Mũ mã Mun manta da ku, kuma ku dãnɗani azãbar dawwama sabõda abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
إِنَّمَا يُؤْمِنُ بِـَٔايَٰتِنَا ٱلَّذِينَ إِذَا ذُكِّرُواْ بِهَا خَرُّواْ سُجَّدًۭا وَسَبَّحُواْ بِحَمْدِ رَبِّهِمْ وَهُمْ لَا يَسْتَكْبِرُونَ ۩ ﴿١٥﴾
Waɗanda ke ĩmãni da ãyõyinMu kawai, sũ ne waɗanda idan aka karanta musu ãyõyinMu sai su fãɗi sunã mãsu sujada kuma su yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinsu, alhãli kuwa su bã su yin girman kai.
تَتَجَافَىٰ جُنُوبُهُمْ عَنِ ٱلْمَضَاجِعِ يَدْعُونَ رَبَّهُمْ خَوْفًۭا وَطَمَعًۭا وَمِمَّا رَزَقْنَٰهُمْ يُنفِقُونَ ﴿١٦﴾
Sãsanninsu nã nĩsanta daga wurãren kwanciya, sunã kiran Ubangijinsu bisa ga tsõro da ɗammãni, kuma sunã ciryawa daga abin da Muka azurta su.
فَلَا تَعْلَمُ نَفْسٌۭ مَّآ أُخْفِىَ لَهُم مِّن قُرَّةِ أَعْيُنٍۢ جَزَآءًۢ بِمَا كَانُواْ يَعْمَلُونَ ﴿١٧﴾
Sabõda haka wani rai bai san abin da aka ɓõye musu ba, na sanyin idãnu, dõmin sakamako ga abin da suka kasance sunã aikatãwa.
أَفَمَن كَانَ مُؤْمِنًۭا كَمَن كَانَ فَاسِقًۭا ۚ لَّا يَسْتَوُۥنَ ﴿١٨﴾
Shin, wanda ya zama mũmini yanã kamar wanda ya zama fãsiƙi? Bã zã su yi daidai ba.
أَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ فَلَهُمْ جَنَّٰتُ ٱلْمَأْوَىٰ نُزُلًۢا بِمَا كَانُواْ يَعْمَلُونَ ﴿١٩﴾
Amma waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwafai, to, sunã da gidãjen Aljannar makõma, a kan liyãfa sabõda abin da suka kasance sunã aikatãwa.
وَأَمَّا ٱلَّذِينَ فَسَقُواْ فَمَأْوَىٰهُمُ ٱلنَّارُ ۖ كُلَّمَآ أَرَادُوٓاْ أَن يَخْرُجُواْ مِنْهَآ أُعِيدُواْ فِيهَا وَقِيلَ لَهُمْ ذُوقُواْ عَذَابَ ٱلنَّارِ ٱلَّذِى كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ ﴿٢٠﴾
Kuma waɗanda suka yi fãsiƙanci to makõmarsu ita ce wuta, kõ da yaushe suka yi nufin su fita daga gare ta, sai a mayar da su a cikinta, kuma a ce musu: "Ku ɗanɗana azãbai wutã, wadda kuka kasance kunã ƙaryatãwa game da ita."
وَلَنُذِيقَنَّهُم مِّنَ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَدْنَىٰ دُونَ ٱلْعَذَابِ ٱلْأَكْبَرِ لَعَلَّهُمْ يَرْجِعُونَ ﴿٢١﴾
Kuma lalle Munã ɗanɗana musu daga azãba, mafi ƙasƙanci, kãfin a kai ga azãba mafi girma, dõmin fãtan za su kõmo.
وَمَنْ أَظْلَمُ مِمَّن ذُكِّرَ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِۦ ثُمَّ أَعْرَضَ عَنْهَآ ۚ إِنَّا مِنَ ٱلْمُجْرِمِينَ مُنتَقِمُونَ ﴿٢٢﴾
Kuma wãne ne ya fi zãlunci bisa ga wanda aka tunãtar da ãyõyin Ubangijinsa, sa'an na ya bijire daga barinsu? Lalle Mũ, Mãsu yin azãbar rãmuwa ne ga mãsu laifi.
وَلَقَدْ ءَاتَيْنَا مُوسَى ٱلْكِتَٰبَ فَلَا تَكُن فِى مِرْيَةٍۢ مِّن لِّقَآئِهِۦ ۖ وَجَعَلْنَٰهُ هُدًۭى لِّبَنِىٓ إِسْرَٰٓءِيلَ ﴿٢٣﴾
Kuma lalle haƙĩƙa, Mun bai wa Mũsã Littafi, sabõda haka kada ka kasance a cikin shakka daga haɗuwa da shi. Kuma Mun sanya shi ya zama shiriya ga Banĩ Isrã'ĩla.
وَجَعَلْنَا مِنْهُمْ أَئِمَّةًۭ يَهْدُونَ بِأَمْرِنَا لَمَّا صَبَرُواْ ۖ وَكَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يُوقِنُونَ ﴿٢٤﴾
Kuma Mun sanya shugabanni daga cikinsu, sunã shiryarwa da umurninMu, a lõkacin da suka yi haƙuri, kuma sun kasance sunã yin yaƙĩni da ãyõyinMu.
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَفْصِلُ بَيْنَهُمْ يَوْمَ ٱلْقِيَٰمَةِ فِيمَا كَانُواْ فِيهِ يَخْتَلِفُونَ ﴿٢٥﴾
Lalle Ubangijinka shĩ ne zai rarrabe a tsakãninsu a Rãnar ¡iyãma a cikin abin da suka kasance sunã sãɓa wa jũna a cikinsa.
أَوَلَمْ يَهْدِ لَهُمْ كَمْ أَهْلَكْنَا مِن قَبْلِهِم مِّنَ ٱلْقُرُونِ يَمْشُونَ فِى مَسَٰكِنِهِمْ ۚ إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَءَايَٰتٍ ۖ أَفَلَا يَسْمَعُونَ ﴿٢٦﴾
Shin, ba ya shiryar da su cẽwa da yawa Muka halakara gabãninsu, daga al'ummõmi sunã tafiya a cikin masaukansu? Lalle a cikin wancan akwai ãyõyi. Shin, ba su jĩ ne?
أَوَلَمْ يَرَوْاْ أَنَّا نَسُوقُ ٱلْمَآءَ إِلَى ٱلْأَرْضِ ٱلْجُرُزِ فَنُخْرِجُ بِهِۦ زَرْعًۭا تَأْكُلُ مِنْهُ أَنْعَٰمُهُمْ وَأَنفُسُهُمْ ۖ أَفَلَا يُبْصِرُونَ ﴿٢٧﴾
Shin, kuma ba su gani ba cẽwa lalle Mũ, Munã kõra ruwa zuwa ga ƙasã ƙeƙasasshiya, sa'an nan Mu fitar, game da shi, wata shũka wadda dabbõbinsu, da su kansu ke ci daga gare ta? Ashe fa ba su gani ba?
وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلْفَتْحُ إِن كُنتُمْ صَٰدِقِينَ ﴿٢٨﴾
Kuma sunã cẽwa, "Yaushe wannan hukunci yake, aukuwa idan kun kasance mãsu gaskiya?"
قُلْ يَوْمَ ٱلْفَتْحِ لَا يَنفَعُ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِيمَٰنُهُمْ وَلَا هُمْ يُنظَرُونَ ﴿٢٩﴾
Ka ce: "Ranar hukuncin nan, ĩmãnin waɗanda suka kãfirta bã zai amfãne su ba (a cikinta) kuma bã zã a yi musu jinkiri ba."
فَأَعْرِضْ عَنْهُمْ وَٱنتَظِرْ إِنَّهُم مُّنتَظِرُونَ ﴿٣٠﴾
Sabõda haka ka kau da kai daga barinsu, kuma, ka yi jira lalle, sũ ma mãsu jira ne.